Ziyarar Mallam Dr. Dikko Umar Radda ga Bankin Raya Africa
Gwamnan Jihar Katsina Ya Ziyarci Bankin raya Africa, Ya nemi tallafin su kan bunkasa harkar Noma, Ilimi da Lantarki. Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, ya ziyarci Bankin Raya Afirka (AFDB) inda ya gana da Babban Daraktan Bankin, Mista Lamin Barrow a ofishin Bankin da ke Abuja a ranar Alhamis, 8 ga watan Yuni 2023. Ziyarar na da nufin tattauna batun saka hannun jari da tallafin shiga tsakanin Katsina da Bankin don taimakawa wajen bunkasa samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’ummar jihar Katsina. Dr Radda, a cikin jawabin nasa, ya ce, "Muna bukatar taimakon Bankin musamman don magance gibin abubuwan more rayuwa na jihar, kamar wutar lantarki." Ya kuma kara da cewa, makamashin da ake sabuntawa ya kasance wani muhimmin ababen more rayuwa da ake bukata domin samun karuwar tattalin arziki a jihar, wanda hakan ya sanya ziyarar ta zama wajibi. Gwamnan ya kuma bukaci Bankin ya ba da goyon baya don bunkasa muhimman amfanin gona, da suka hada da auduga da ayyukan